LABARIN WANI BABARBARE DA MAGAJI (MAI UNGUWAR FILANI)
Nan Kudancin Kaduna aka ba wani Bafilatani sarautar Magaji, ana nan, sai wani Babarbare ya zo garin, yadda ka san Ibilis haka yake, saboda duk wani hali da Marigayi Abubakar Imam ya bayar na Ja’iru ɗan masa jannati a littafin Magana Jari Ce, ɗan Barebarin ya dama shi ya shanye. Ya ci kayan boka ya ci na malami, ya ci na mai ƙaramin ƙarfi, ya ci na mai salla ya ci na mara salla. Ga shi da tsoron tsiya ko farar kura albarka. Ba abin da ya fi ba jama’ar wurin haushi sai rintonsa, ga sata sai ka ce burgu, kai ko abin da ba a so ne, matuƙar ya san ranka zai ɓaci in ya ɗauka, to, zai aikata haka. Kai ko bola ce zai ɗauka in ya yi gaba ya zubar, shi bai sami komai ba kai kuma ka rasa.
Ana nan, ka san halin ƙabila ba shi da yafiya, faɗa ya haɗa shi da wasu ƙabilu, su kuwa suka ce da wa Allah ya haɗa su ba da shi ba. Nan da nan, duniyar ta yi masa ƙunci. Ya yi nan su tare, ya bi nan su tare. Ya dai tabbatar da mutuwarsa ta so, don ga shi tana gewaya shi. Nan da nan ya rugu wurin Sarkin Filani Magaji, ya roƙe shi Allah, annabi, a taimaka masa kada ya rasa ransa. Shi dai fatar sa a kira ƙabilun nan a yi sulhu. Da ma Magaji na tunanin yadda zai da shi sai ga dama ta samu.
Magaji ya aika aka kira ƙabilun suka zo aka zauna shari’a, ya kalli na farko da ke ta zaƙewa ya ce, “Kai wace ƙabila ce?”
Ya ce, “Yallaɓoi, ni Jaba ne.”
Magaji ya kalle ya ce, “To, ja baya, da manyanka za a yi.” Na biyun ya matso yana murna ya ji an ce ba za a yi da Jaba ba. Magaji ya kalli na biyun ya ce, “To, kai kuma fa?”
Ya ce, “Ni Kaje ne Allah Ya taimake ka.”
Magaji ya yi shuru, sannan ya nisa ya ce, “To, maza je ka, ba ma son ganin ka a nan.” Sai na ƙarshe ya matso yana wani kumbure-kumbure. Magaji ya dube shi ya ce, “Kai ma da kai ne?”
Ya amsa da, “Eh yallaɓoi!”
Magaji ya ce, “Wace ƙabila ce kai?”
Ya ce, “Ni Kataf ne.”
Magaji ya ce, “To, ka tafi ɗin.” Daga nan ya juya ya kalli ɗan Barebare duk ya shiga taitayinsa. Ya ce da shi, “Kai kuma fa?”
Ɗan Barebare ya zabura zai gudu, sai da aka rirriƙe shi, sauran ƙabilun suka ji daɗi, don suna ganin ƙarshen sa ya zo. Cikin fargaba da sanyin murya ya ce, “Ni Barebari ne!”
Magaji ya ce, “To, maza ka bar garin nan shekara goma. Maza ka yi Gabar shekara goma na ce.” Ƙabilu suka yi ihu alamun sun ji daɗin wannan hukunci da aka yi wa Barebari. Wannan shi ne dalilin da ya sa a garin Kaduna ba Barebari da yawa duk sun yi Gabar ɗin sai masu taurin kai da suke ɗan dawo a ɓoye bayan wa’adin da aka ba su. Kuma ba su cika son ana tayar da wannan taɗin ba, saboda ana yi masu dariya. Yaran Barebari ne kawai ba su san wannan labarin ba. Amma duk Babarbare mai shekara arba’in ya sani.
Comments
Post a Comment