Skip to main content

Posts

Showing posts from November, 2021

Ba sata ke da ciwo ba, a maida mutum wawa:

Ba sata ke da ciwo ba, a maida mutum wawa:  Wani mahaukaci ne ya samo dawonsa guda biyu irin wanda ake mulmulawar nan da girma ya ajiye ko me yake jira oho, ya ɗan dai fita.  To, kafin ya dawo sai wani mara tsoron Allah ya zo ga dowon sai ya sace ɗaya, ɗayan kuma da ya bar masa sai ya raba biyu ya mulmula kowane sai suka zama biyu amma fa ƙanana, ya tafi abinsa.  Ko da mahaukacin nan ya dawo ya ga abin da aka yi masa sai ya tsaya shuru. Yana faɗin, “Ni dai ba satar da aka yi mani ba wayau da aka raina mani shi ya fi ciwo.”  Watau ana ganin kamar bai san abin da ya ajiye ba ne.

“Allah Ya yi Allahu Nasa, Bamaguje ya ishe biri ya mutu a gonarsa.”

“ Allah Ya yi Allahu Nasa, Bamaguje ya ishe biri ya mutu a gonarsa.” Ƙabilar Maguzawa mutane ne mafarauta kuma cikin abin da suka fi so su farauta har da birai, to, yawan farautarsu da suke yi ya sa har biran sun gudu su shiga daji inda ba kowa ba ne zai iya zuwa wurin.  Ka san ba yadda Allah bai iya ba, wata rana ya daɗe rabonsa da ya farauci biri sai ya je gonarsa gewaya kawai sai ya samu biri matacce a gonar, wanda shi a nasa ɗabi’ar zuwa farautarsa yake yi sai ga shi banza ta faɗi, don haka cikin irin murnar da zai yi shi ne yake cewa: “Allah Ya yi Allahu Nasa.” Da yake lokacin Musulunci ya bayyana a ƙasar; ya ɗauko kayansa ya kawo gida suka sha dabge.  Mutane kuma da suka ji wannan labari sai duk wanda irin wannan abin farin ciki ya sama na ba zata sai shi ma ya ce, “Allah Ya yi Allahu Nasa.” Sai ka ji waɗanda suka san labarin suna ƙarasa masa da cewa, “Bamaguje ya ishe mushen biri a gonarsa.” Akwai magana, an mari ɗan Bamaguje. Ana ta Maguzawanasali wa yaketa su Ciwak

LABARIN KARIN MAGANA: A Sa A Baka Ya Fi A Rataya

A sa a baka ya fi a rataya:  Kura ce yunwa ya sa ta shiga gari da dare, da za ta shiga sai ta wuce ta wani rugar filani amma sun tashi, ta duba ba ta samu komai ba sai wani ɗan ƙaramin akuya, mara lafiya, sun ɗauka ma ya mutu ne, suka bar shi.  Kura ta yi tsaki ta wuce tana tunanin gaba za ta samu mai mai  kuma ta raina wannan da ta samu. Ta shiga gari ta ƙaraci yawonta ba ta samu komai ba, sai ta dawo za ta koma, ta ma manta da ta yi gamo a farkon shigowarta. Ko da ta zo ta wuce rugar sai ta tuna da ta yi tsintuwaa da. Sai ta juyo ta samu wannan ɗan maraƙin tana faɗin a sa a baka ya fi a rataya.

LABARIN KARIN MAGANA: ALBISHIRINKU MAHASADA MAGANINKU CARBI

Albishinku mahasada maganinku carbi:  An ce wai a zamanin Sardauna, ya taɓa ziyartar shahararren Sarkin nan na Habasha Sarki mai zakuna, wanda a yadda ake faɗa shi ba ka isa ka shiga fadarsa sannan in za ka fito ka juya masa baya.  Sai dai ka fito kana tafiya da baya da baya.  Amma kana juya masa baya zai sa zakuna su kashe mutu.  To bayan Sardauna ya gama yin abin da zai yi a fadar ko da ya tashi sai ya juya ya ci gaba da tafiyarsa. Sarki mai zakuna ya ga ba zakin da ya yi nufi ya farmaki Sardauna balle su kashe shi. Sarki ya yi masu ishara amma a banza suna nan a mazauninsu. Ya yi duk ƙoƙarin da zai yi don dai ya ga sun gama da Sardauna amma duk a banza.  Har daiSardauna ya kai ƙofar fita fadar sai ya juyo ya dawo da ya kawo wurin Sarkin sai ya nuna masa carbinsa sannan ya juya ya tafi abinsa. Shi ne ake karin maganar, albishirinku mahasada maganinku carbi.

Labarin: Ba na sayarwa ba ne, ya gagari Kundila

Ba na sayarwa ba ne, ya gagari Kundila:  Kundiya wani attajiri ne da ya shahara a garin Kano ya zauna na a unguwar Makwarari, shi ne aka ce bai san yawan bayinsa da ke zaune a cikin birni ko kanyukan Kano ba.  Da Kundila ya ga ya bunƙasa haka, sai idan ya fito majalisarsa da yamma duk wani abin da aka zo wucewa da shi, da zuciyarsa ta mila sai ya ce a kawo, abin nan kuwa ko da kashi ne, zai ce a yi masa kuɗin tsiya ya biya.  Wata rana sai ga wata tsohuwa ta yo itace za ta kai gida, Kundila ya sa aka kira ta ya ce zai saya ta ce, “wannan ya fi ƙarfinka, ba za ka iya saya ba.” Shi ko ya nace sai dai ta yi kuɗin tsiya shi ko ya biya. Buɗar bakin ta sai ta ce, “Bana sayarwa ba ne.” Cikin 'yan kanzagin da ke zaune sai wani ya ce, “Ya ko gagari Kundila.”  Don ko, Kundila ba Basarake ba ne balle ya nuna karfin mulki, kuma ba ɓarawo ba ne ko ɗan fashi balle ya ƙwata ko ya sace.

Labarin Gaba Ta Kai Ni Gobarar Tti Jos

Gaba ta kai ni, gobarar Titi a Jos:  Wata tsohuwa ce mai suna Titi a garin Jos ba ta da komai sai ’yan tarkace irin na tsofoffi. Rannan ba ta nan sai gobara ta tashi a ɗakinta kafin ta dawo wuta ta cinye komai.  Ko da Tti ta dawo ta rasa abin yi ta yi kuka har ta gode Allah. Tana nan zaune ta rasa abin yi sai makwabta da sauran abokan arziki da suka ji abin da ya faru da ita, sai  suka shiga zuwa yi mata Allah ya kyauta, kuma kowa ya zo ba ya zuwa hannu banza kafin ka ce me? Allah Ya mayar wa Titi abin da ta rasa ninkin ba ninkinsa.  Sai ga shi ta kama murna tana cewa “Ai wannan gobara gaba ta kai ni.” Shi ke nan ya zana karin magana da ka faɗa sai ka ji ana ƙarasa maka da “Gobarar Titi a Jos”  

Labarin Karin Magana: Aiki da hankali ya fi aiki da agogo:

Aiki da hankali ya fi aiki da agogo:  Akwai wani baƙo da ya taɓa ziyartar wani Sarki, sai kullum ya zo fada ya zauna in an tashi ya tashi ya tafi. Rannan sai Sarki ya ce da shi wai kai meye aikin ka? Sai baƙo ya ce shi aikinsa, shi ne aiki da hankali!  Sarki ya ce ni ko ina so ka yi mani aiki da hankali. Baƙo ya ce shi ke nan. Aka kwashi watannan Sarki bai ga ya ce da shi komai ba, har Sarki ya gaji ya tambaye shi. Sai mai aiki da hankali ya ce, idan na yi ma aiki da hankalina za ka sa akashe ni ne! Sarki ya ce  aikin banza daga kawai ka yi abin da na saka sai in sa a kashe ka? Ina nan ina jirar ka ka yi aikin da hankalin naka.  Sarki ya takura wa ma aiki da hankali sai mai aiki da hankali ya ce, to, a tara malamai. Sarki ya rantse da cewa duk abin da ya faɗi ba zai  yi masa komai ba. Sarki ya sa aka tara Malamai ya yi rantsuwa a kan cewa duk abin da mai aiki hankali ya faɗi bai da wata uƙuba.  Sai mai aiki da hankali ya ce, ran nan muna zaune ka sa an je an sayo dawakai ha

Labarun Karin Magana: Kunar Bakin Wake

Ƙunar Baƙin-wake:  Wai, a Katsina aka yi wani da ake kira Baƙin-wake, a zamanin irin lokacin nan ne da sarakuna ke yin abin da suka ga dama da mutanensu. Sarkin lokacin shi bai da wata ɗabi’a a lokacin hawa sai ya samu ma-jiya-ƙarfi ya hau bayansu, shi da yaransa a yi ta yawo shi haka yake hawansa ba a kan doki ba.  To, shi Baƙin-wake abin ya dame shi har ya yi wa kansa alƙawarin cewa, a duk ran da abin ya kawo kansa ya zo ƙarshe, amma sai ya yi bakam ya ƙi faɗa wa kowa mugun tanadinsa,  aka ko yi sa’a da lokacin hawa ya yi sai aka zaɓa har da shi  cikin waɗanda za a yi hawa da su.  Baƙin-wake bai kula ba aka ga ma sai murnarsa yake yi. Ashe da abin da ya shirya. Ko da lokaci ya yi aka shirya aka fita hawa, me zai faru Baƙin-wake shi ke ɗauke da Yarima mai jiran gado aka biyo ta wata maƙera babba ga mutane nan sun zagaye ta sai zuga suke ta yi ga wuta nan  ba daman ka yi kusa, ko da Baƙin-wake ya hango sai ya ƙara taku ya ba waɗanda ke bin sa tazara aka ga gadan-gadan ya nu

Wakar Sarkin Zazzau Alhaji Shehu Idris ta Adam A Zango

Adam A. Zango Sarkin Zazzau Hanjin Jimina Sanƙira : Gyara kimtsi, : Gaba salamun baya salamun. : Hadari sa gabakanka inda kake so Yariman Mawaƙa, : Mu je zuwa, aha! Jagora: Adam Zango mai gari, : Yaro ne adon gari, : O’o o, o’o o, oo, Sanƙira: Toh, toh, to! Amshi: Ga kambun mafarauta, : Dogon barde hancin giwa. Jagora: Ga mai darajar farko matsayi, : Sarkin Zazzau hanjin jimina, Karɓi: Kowa ya ci sai ya lalace, : Matsayinka daban babban sarki. Jagora: Kai duk tsananin ramar doki, Karɓi : Kofato na nan bai ramewa, : Haka Rabbi yake aje hikimarsa, Jagora: To ga Sarkin Zazzau, : Shehu Idiris mai takalman ƙare, : Toh, Amshi: Ga kambun mafarauta, : Dogon barde hancin giwa. Jagora: Ga mai darahar farko matsayi, : Sarkin Zazzau hanjin jimina, Karɓi: Kowa ya ci sai ya lalace, : Matsayinka, Jagora: Um! Karɓi : Daban babban sarki. Jagora : Ga mai ƙarfi Dagacin mutuwa, Karɓi : Sankace da maciji dauji kar, : Sarkin Zazau tafiya sannu, Jagora : Um! Karɓi

YADDA SARKI FALAMA YA RASA DALOLINNSA NA YOUTUBE II

YADDA SARKI FALAMA YA RASA DALOLINNSA NA YOUTUBE II Tambaya:  Falama kwana biyu ya batun YouTube? Falama:  YouTube ana nan ana ba da himma. Tambaya: Kwanaki da yawa masoya sun ji ka shuru a tashar FALAMA TV, ba waƙa sannan ka fara sanya wani fim na HAUSA COMEDY mai suna GIDA ƊAYA amma kuma sai aka ji shuru? Falama: Sawun giwa ne ya take na raƙumi. Ka san duk cinikin da kake yi wata rana ka sa ran faɗuwa; ko a kasa ba a sayar ba. Batun Falama TV ina mai ba wa masoya haƙuri. Ka san YouTube rainonsa ake yi don a sami kuɗi; suna da nasu ƙa’idojin da suke buƙata ka cika su kafin su fara biyanka. To, da yawa akan sami matsala wurin cika waɗannan ƙa’idoji, wanda Tashar Falama TV ita ma ba ta ma ba ta ƙetare waɗannan matsalolin ba. Tambaya: Sarki sai na ga da na duba tashar FALAMA TV tana da SUBSCRIBERS DUBU ƊAYA DA ƊARI BIYAR da VIEWERS DUBU ƊARI DA SABA’IN DA BAKWAI DA ƊARI DA SABA’IN DA BAKWAI kuma har a yanzu ma ana ganin tasharka a a gida Nigeriya da Nijar da Libiya da S

YADDA SARKI FALAMA YA RASA DALOLINNSA NA YOUTUBE I

YADDA SARKI FALAMA YA RASA DALOLINNSA NA YOUTUBE I Tambaya:   Za mu so mu ji sunan baƙon namu duk da cewa sananne ne? Falama: Sunana Muhammad Bello Falama wanda aka fi sani da Sarki Falama a dandalin Facebook ko zaurena na sarkifalamablogspot.com ko a Twitter ko a Linkedin. Ɗalibin digirin MA ne a African Literature a Sashen Harsuna Da Al’adun Afirka a Jami’ar Ahmadu Bello da ke Zariya. Tambaya:  Sarki Falama ke nan; Digirin Em’en nan fa Masters yake nufi.  Sarki muna yi maka fatan alheri da kuma fatan kammalawa cikin nasara.  Ga waɗanda ba su sani ba Sarki Falama shi ne mamallakin shafin nan na Facebook da ake kira HAUSA KARIN MAGANA  – har wa yau; shi ne mamallakin zauren nan na sarkifalamablogspot.com mai suna SARKI FALAMA da yake kawo mana abubuwan da suke na Hausa da Hausawa  kuma kankat shi ne mamallakin tashar nan ta YouTube da ake kira FALAMA TV  WANDA A YAU ZA MU TATTAUNA NE DA SHI A KAN WAƘOƘIN MAWAƘANMU NA DAURI DA YAKE SHIFTARSU YANA SANYA SU A TASHAR FALAMA T

ko kun san?

Kuratandu

Film Sai Dan Fim

Fim Sai Dan Fim

Bunkasar Rubuce-Rubucen Hausa

Wasu Ababe Na Daban Da Suka Taimaka Wurin Bunƙasar Rubuce-Rubucen Hausa Tun daga lokacin da Allah Ya ƙaddara na’urar kwamfyuta ta yawaita, sai rubuce-rubuce ya ƙara sauƙaƙa ga marubuta, ta yadda za ka ga wani ma ya mallaki tasa ta kansa, don haka, ya zauna ya tsara littafi ba wata wahala ba ce tun da, da ma rubutu da na’ura shi ne mataki na cewa an ɗaura ɗambar buga littafi. Kuma wasu ababe da suka ƙara taimakawa wurin bunƙasar rubuce-rubuce sun haɗa da: An samun da yawa daga cikin al’umma da suka iya rubutu da karatu. Kakkafa ƙungiyoyin marubuta daban-daban. Samuwan kamfanoni masu buga littattafai da tallata su. An samu shagunan sayar da littattafan da ake bugawa a ko’ina. Gidajen rediyo da ke ware filiye na musamman domin karanta littattafan marubuta da kuma yin hira da su. Yadda da yawa daga cikin matasa sun samu sha’awar rubuce-rubuce da kuma mayar da shi sana’a. Yadda baƙi ke zuwa daga wasu ƙasashe domin sayan littattafan marubuta su yaɗa su. Gasanni da ake ƙoƙarin shi