Skip to main content

adamu zango

Adam A Zango
Adamu Zango Mai Zamani
Amshi : Yaro adon gari,
: Adamu Zango mai zamani,
: Fasa taro.
Jagora : Ni ne adon gari,
: Matar aure ’yar asali,
: Zan zaɓa...
: Bisimilla Sarkina,
: Allah Mai biyan buƙata,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Taimaken Allah,
: Nai mata mai hali da tsafta,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Na saka ka a farko,
: Rabbani Walla bai buƙata
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Ɗan Abdalla ba na shan wahala,
: Mai ado da kufta,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Rabbi kai kay yarje mui aure,
: Don mu je mu huta,
Amshi : Yaro adon gari,
: Adamu Zango mai zamani,
: Fasa taro.
Jagora : Yau gashi ina so nai aure,
: Auren addini,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Na sauka a Barno neman aure,
: Wata ɗiya ta gan ni,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Ta ce mani “indawatu”
: Adam taho gare ni,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Sai na ce, “kele wasile”
: Aure na zo ku ba ni,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Na ji an ce kuna ado da tilare,
: Na ke ce raini,
Amshi : Yaro adon gari,
: Adamu Zango mai zamani,
: Fasa taro.
Jagora : Na ce, “yaya sunanki,
: ’Yanmata mai diri da sura”
Karɓi : Sunana Falmata,
: Yarinyar da ba ta yin fitsara,
: Mu je gida ka gaida iyayena,
: Don kar kai min dabara,
: Idan kana da Naira ɗan Sarki,
: Ka zo mu je a ɗaura,

Jagora : Wayyo ’yanmata ni ba ni da Naira
: Yauna za ni na haura,
: Yanzu,
Amshi : Yaro adon gari,
: Adamu Zango mai zamani,
: Fasa taro.
Jagora : Sai na sauka a Yola,
: Tashan mota zan wuce Jimeta,
: Na ɗauki jaka zan tsallaka titi,
: Duk na jigata,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Ga ƙishi da yunwa ta dame ni,
: So nake na huta,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Sai na ga rijiyar burtsatai,
: Mata sun kewaye ta,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Kyakkyawa na cikinsu,
: Ta ba ni kofi na ruwa mai tsafta,
: In sha,
Amshi : Yaro adon gari,
: Adamu Zango mai zamani,
: Fasa taro.
Jagora : Sai ta ce da ni, “use”,
: Sai na amsa,
: Sai tai min murmushi na duba,
Karɓi : Kai kaɗo yaya sunanka,
:Ba na na ƙirƙiro ba.
Jagora : ’Yar Fullo,
: Sunana Adam Zango,
: Aure na zo na duba,
Karɓi : Ni ma dai bari ka ji sunana,
: Sunana Habiba,
: Sai kana da garken shanu,
: Za ka auri Habiba.
Amshi : Yaro adon gari,
: Adamu Zango mai zamani,
: Fasa taro.
Jagora : Ni ba ni da ko garken shanu,
: Naija za ni koma,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Ga ni nan a Naija garin Nufawa,
: Ina ta himma,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Ina da aboki a Fandulu,
: Da ƙanwarsa Karima
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Ya kai ni gidansu ya ba ni abinci,
: Sakwara da nama,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Ya ce ga Karima ta ba ni ruwa,
: Mai sanyi da ni’ima,
: Na sha,
Amshi : Yaro adon gari,
: Adamu Zango mai zamani,
: Fasa taro.
Karɓi : Adam zango uko kewano,
: Mai ka zo garinmu?
Jagora : Ƙanwata ina neman aure,
: Shin ko za ni samu?
Karɓi : Yayana shin kana son wace ce,
: A nan cikin garinmu?
Jagora : Ko ke zan aura ba komai,
: In har za a samu,
Karɓi : To za ka noma kunya dubu na doya,
: San nan ka samu!
Jagora : A’a ba zan iya ba na haƙura,
: Zan je Kano ta Dabo,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Ga ni ƙasar Kanawa Ƙofar Mata, 
: Ina ta ƙwambo,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Sai ga wata bebi kyakkyawa,
: Ta sayi akumbo,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Ta sanya atamfa ta sha lalle,
: Tana ta bobo,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Muka haɗa idanu ni da ita,
: Muka yo kwalabo,
: Sosai,
Amshi : Yaro adon gari,
: Adamu Zango mai zamani,
: Fasa taro.
Jagora : Nan na ce mata ’yam mata,
: Don Allah na tambaye ki,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Na ga kyan diri kyawu da mutunci,
: Suna gare ki,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Na zo neman aure,
: Wane unguwa zan zo na gan ki,
Karɓi : Ni ’yar Gwammaja ce ’yar malam,
: Mai hali na kirki,
: In kana da haddan Ƙur’ani,
: Aurenmu babu burki,
: Ka ji,
Amshi : Yaro adon gari,
: Adamu Zango mai zamani,
: Fasa taro.
Jagora : Ni ba ni da hadda,
: Na sauke kuma na san hadisi
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Sai na sauka Zazzau,
: Birnin Shehu jikan Sunusi,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Na sauka a Gyalle,
: A wurin Alin Taro da Sisi,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Yana da shago na yin ɗinki,
: Mai ado da fansi.
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Sai ga wata kyakkya ta shigo,
: Mai asali na jinsi,
Amshi : Yaro adon gari,
: Adamu Zango mai zamani,
: Fasa taro.
Jagora : Na ce assalamu alaiki,
: ’Yam mat azan so na gan ki,
Karɓi : Wa alaikas salam Adam Zango,
: Na kawo maka ɗinki,
Jagora : A’a ba ni ɗinki ’yam mata,
: Ƙauna na zo na ba ki,
Karɓi : Aure ka zo mu yi ko ko soyayya,
: Gidanmu kai sadaki,
Jagora : Ta kai ni wurin abbanta,
: Dattijo ne yana da kirki,
Karɓi : Tambaya ta farko yaro,
: Kai ɗan wane gari ne?
: Kai ɗan wane ne kuma,
: Kai ɗan wane jinsin yare ne?
Jagora : Babana Ibrahim kuma ɗan Abdalla,
: Maƙerin nan ne,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Bahausen Zango ne ni,
: Baba ka je Fada za ka gane,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Sana’ata wasan Hausa,
: Da waƙa ɗan gidan malamai ne,
Karɓi : Yaro ka je ka turo iyayenka,
: Ni na ba ka Zainab,
Jagora : Wayyo baba ya ba ni Zainab,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Wayyo an ba ni Zainab,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Sosai an ba ni Zainab,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Ina son ki Zainab,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Ina ƙaunarki Zainab,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : I lobyu Zainab,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Na samu Zainab,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Yau baba ya ba ni Zainab,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Wayyo an ba ni Zainab,
Karɓi : Lale lale.
Jagora : Sosai an ba ni Zainab,
Karɓi : Lale lale.














Adam A Zango
Wayyo Ni Ina Son Ta
Jagora : Oh!
Karɓi : Wayyo!
Jagora : Ni ina son ta
Karɓi : Ni ina son ta,
Jagora : Wayyo!
Karɓi : Wayyo!
Jagora : Ni ina son ta,
Karɓi `: Ina son ta,
Jagora : Shuhuda,
: I lobyu Shuhuda
: Shuhuda,
: I lobyu Shu Shu Shu,
Jagora : Wata rana na haɗa kayana,
: Zan yi tafiya na yi shirina,
: Na ɗau ado za ni Abuja,
: Wurin buki na abokina,
: Na ga jama’a duka sun taru,
: Kowa da kowa na murna,
: A cikinsu na yi gamo da katar,
: Don tafiya mai ban sha’awa,
: Yarinya Shuhuda,
Karɓi : Shi yana son ki,
Jagora : Son ki ya,
Karɓi : Shiga rihinshi.
Jagora : Jalla kai ni,
Karɓi : Muradina,
Jagora : Eh, Shuhuda ki zan tawa,
: Ɓatad da kama daga Indiya,
: Da ɗaiɗaya taka takawa,
: Ta ɗau mayafi ta sanya,
: Jikinta duk ta yi rufewa,
: Sannan ga ta doguwa,
: Madaidaiciya ba kushewa,
: Adamu dai a tunanina,
: Budurwa ce mai hangowa,
: Na tambayi matar abokina,
: Sunanta daure ta gaya min,
: Wancan shin wace ce,
: Sunanta daure ki gaya min,
: Kamalarta da kimarta,
: Da shigarta biyu duka sun... 
: Ina son ta da niyyar aure,
: In har ko ta lamunce min,
: Ta ce mun sunanta Shuhuda,
: Amma da Shu za ka sanin,
: Kwana biyu ya rage aurenta,
: Ina nufin an ba da ta,
: Dagan an sai nac ce na haƙura,
: A zuciyata na cire ta,
: Na bi umurnin Musulunci,
: Na dangana daga narkewa,
: Yarinya Shuhuda,
Karɓi : Yana son ki,
Jagora : Eh, son ki ya,
Karɓi : Shiga ruhinshi,
Jagora : Jalla kai ni,
Karɓi : Muradina,
Jagora : Eh, Shuhuda ki zan tawa,
: Tun a lokacin da na dawowa,
: Da safe gari ya wayewa,
: Na je ni jungun ummata,
: Zai gai da ita nai duƙawa,
: Sai ta gwadan hoton Rashida,
: A bayan mun gama gaisawa,
: Sai ta ce in aure ta,
: Hankalinta za ta fi kwantawa,
: Nan take na’ amsa batunta,
: Don faranta mata rayinta,
: Da na je na ga Rashida, 
: Ni da ita sai muka daidaita,
: Anka ɗaura mana aure,
: Zaman lafiya muke ni da ita,
: Ba faɗa ba janjani,
: Junanmu ba mai kokawa,
: Hat ta kai mu ga mun haihu,
: Muka samu mai sunan baba,
: Yarinya Shuhuda,
Karɓi : Yana son ki,
Jagora : Eh, son ki ya,
Karɓi : Shiga ruhinshi,
Jagora : Jalla kai ni,
Karɓi : Muradina,
Jagora : Eh, Shuhuda ki zan tawa,
: A kwana a tashi kwatsam,
: Matar abokin nan nawa,
: Na fito daga aikina,
: Ni da ita sai munka haɗewa,
: Ita ce ta gayan cewa,
: Shuhuda dai ta yi fitowa,
: Kuma tana ta nema na,
: Lambar wayar ba ta shigowa,
: Nan take na ce mata to,
: Ko za ki ban lambarta,
: Ta ce mini ba komai,
: Zan ba ka har adireshinta,
: Ta ɗauka tab ba ni,
: Da zuwa gida na yi kiranta,
: Sunana Adamu Zango,
: Kalma ta farko da na furta, 
: Buƙatata ki amince da ni,
: Aure na ƙauna mu ƙullawa,
: Ta yi dogon numfashi,
: Da ya sanya raina ya bugawa,
: Ta ce in mata uzuri,
: Za ta je ta yi shawartawa,
: Sai ta ce amma in sani,
: Ƙauna da ni ta yarjewa,
: Sai na ce mata ba komai,
: Na yarda na yi amincewa,
: Na yi karo da abun ƙauna,
: Mai hankali ’yar Larabawa,
: Eh, yarinya Shuhuda,
Karɓi : Yana son ki,
Jagora : Eh, son ki ya,
Karɓi : Shiga ruhinshi,
Jagora : Jalla kai ni,
Karɓi : Muradina,
Jagora : Eh, Shuhuda ki zan tawa,
: Ya Shuhuda ’yar asali,
: Haskenki tamkar ya na zara,
: Daure ki amince da ni,
: Don in samu shiga tsara,
: ’Yar Larabawa mai asali,
: Shuhuda mai kyawun sura,
: Mai dashe na farin ƙauna,
: Zan so in so....
: Eh, yarin Shuhuda,
Karɓi : Yana son ki,
Jagora : Eh, son ki ya,
Karɓi : Shiga ruhinshi,
Jagora : Jalla kai ni,
Karɓi : Muradina,
Jagora : Eh, Shuhuda ki zan tawa,
: Shuhuda madubina,
: Abin tunanin ruhina,
: Na kamu da ƙaunarki,
: Har ta sauya tunanina,
: Daure ki amince da ni,
: Shuhuda mui auren ƙauna,
: Na sunna mu yi rayawa,
: Har jama’a su yi ta yabawa,
: Eh, yarin Shuhuda,
Karɓi : Yana son ki,
Jagora : Eh, son ki ya,
Karɓi : Shiga ruhinshi,
Jagora : Jalla kai ni,
Karɓi : Muradina,
Jagora : Eh, Shuhuda ki zan tawa,
: Ya Shuhuda abar so na,
: Kanki kaina ya zautu,
: Sai ki nunan soyayya,
: Hakan ko lallai ya kyautu,
: ’Yan samari na kuka,
: A ba su ke wai sun bautu,
: Sai na ce duka sui haƙuri,
: Tun da dai ta zan tawa,
: Eh, yarin Shuhuda,
Karɓi : Yana son ki,
Jagora : Eh, son ki ya,
Karɓi : Shiga ruhinshi,
Jagora : Jalla kai ni,
Karɓi : Muradina,
Jagora : Eh, Shuhuda ki zan tawa,
: Kanki na yo kokawa,
: Ina zubar da hawayena,
: Don na cimma buƙatuna,
: Aurenki shi ne burina,
: Na so Shuhuda ’yar asali,
: Har wasu jama’a na zagi na,
: Ni fa lallai burina,
: Shuhuda dai ta zamo tawa,
: Eh, yarin Shuhuda,
Karɓi : Yana son ki,
Jagora : Eh, son ki ya,
Karɓi : Shiga ruhinshi,
Jagora : Jalla kai ni,
Karɓi : Muradina,
Jagora : Eh, Shuhuda ki zan tawa,
: Yarinya Shuhuda ina son ki,
: Son ki ya shiga ruhina,
: Jalla kai ni muradina,
: Shuhuda ki zan tawa,
: Eh, yarin Shuhuda,
Karɓi : Yana son ki,
Jagora : Eh, son ki ya,
Karɓi : Shiga ruhinshi,
Jagora : Jalla kai ni,
Karɓi : Muradina,
Jagora : Eh, Shuhuda ki zan tawa,
: Eh, yarin Shuhuda,
Karɓi : Yana son ki,
Jagora : Eh, son ki ya,
Karɓi : Shiga ruhinshi,
Jagora : Jalla kai ni,
Karɓi : Muradina,
Jagora : Eh, Shuhuda ki zan tawa.

Adam A Zango
Wayyo Kai Wannan Zamani
Jagora : Wayyo! 
: Wayyo kai wannan zamani, 
Jagora : Iyayen zamani, 
Karɓi : Wannan zamani.
Jagora : Wayyo! 
: Wayyo kai wannan zamani, 
Karɓi : Wannan zamani.
Jagora : Iyayen zamani, 
Karɓi : Wannan zamani.
Jagora : Matasan zamani,
Karɓi : Wannan zamani.
Jagora : ’Yam matan zamani,
Karɓi : Wannan zamani.
Jagora : ’Yan siyasan zamani,
Karɓi : Wannan zamani.
Jagora : Malaman zamani,
Karɓi : Wannan zamani.
Jagora : Masu kuɗin zamani,
Karɓi : Wannan zamani.
Jagora : ’Yan fim ɗin zamani,
Karɓi : Wannan zamani.
Jagora : Har ma da mawaƙan zamani,
Karɓi : Wannan zamani.
Jagora : Ku buɗe kunne ku ji,
: Waƙar Jatau mai magana,
: Ni ne likitan wannan zamani,
: Mai warƙar da cutar zamani,
: Jatau, uh! Uh!
: Wayyo, uh! Uh! Uh!
: Uh! Uh!
: Wayyo, uh! Uh! Uh!
: Allah mai zamani,
: Kuma shi ne zai mana magani,
: Allah mai zamani,
: To a daina zagin zamani,
: Rami rami na shiga,
: Ramin kura na shiga,
: Ramin damusa na shiga,
: Ramin ɓauna na shiga,
: Ramin alade na shiga,
: Ramin jaki na shiga,
: Ramin zaki na shiga,
: Amma zaki bai bar ni ba,
: Uh! Uh!
: Wayyo, uh! Uh! Uh!
: Kur uh! Uh! Uh!
: Uh! Uh!
: Wayyo, uh! Uh! Uh!
: Ramin kura na shiga,
: Labarin sai ku tsaya ku ji,
: Mutuwar aure a Hausawanmu,
: Abin har na gaji,
: Ina yin rangaji,
: Malamai a kawo agaji,
: Dangi-dangi na shiga,
: Babu dangin da babu bazauwara,
: An yo aure na zumunci,
: Jama’a ga auren ya rabu,
: An yo aure na soyayya,
: Jama’a auren ya rabu,
: An yo aure na dukiya,
: Jama’a aure ya rabu,
: An yo aure na ƙiyayya,
: Jama’a aure ya rabu,
: Jama’a ku biyo ni,
: Jatau yau za na ba ku magana,
: Haƙuri ne magana,
: Ilimin mata magana,
: Tarbiyyan mace magana,
: Ko da namijin bai yi shi ba,
: Uh! Uh!
: Wayyo, uh! Uh! Uh!
: Kur uh! Uh! Uh!
: Uh! Uh!
: Wayyo, uh! Uh! Uh!
: Malamanmu na zamani,
: Sai mu juya kallon zahiri,
: Ɗan wancan ƙungiya,
: Ya ce wa wancan kafiri,
: Shi ma ɗan ƙungiyancan,
: Ya ce wa wancan kafiri,
: To wai wa za mu bi,
: Ku faɗa mana kar mu tsaya jiri,
: Musulunci dai guda ce,
: Ba bambanci a zahiri,
: Jatau mai magani,
: Ku biyo ni zan ba ku magani,
: Tutan Manzon Allah,
: Annabi shi ne zamani,
: Ƙur’ani kalmal Allah,
: Littafi zamani,
: Uh! Uh!
: Wayyo, uh! Uh! Uh!
: Kur uh! Uh! Uh!
: Uh! Uh!
: Wayyo, uh! Uh! Uh!
: ’Yan siyasan zamani,
: Ku yi koyi da riƙon gaskiya,
: Talakawan zamani,
: Sun same ku da zuciya ɗaya,
: Sai ku yi adalci,
: In kun hau ku riƙe su da gaskiya,
: Kar ku manta sai da talakka,
: Mulkinku zai taffiya,
: In kau babu talakka,
: Mulkinku zai sankuya,
: Ah weye!
: Uh! Uh!
: Wayyo, uh! Uh! Uh!
: Kur uhu! Kur uhu!
: Eyee ye yee
: Wannan wanan wannan zamani,
: Allah ka tsare mu da zamani,
: Ƙarya wannan zamani,
: Hassada wannan zamani,
: Gulma a wannan zamani,
: Cuta wannan zamani,
: Sata wannan zamani,
: Yaudawara wannan zamani,
: Allah Ka tsare mana zamani,
: Uhu, Allah ka tsare mana zamani,
: Jatau, ni ne Jatau mai magani,
: Jatau, ni na ba ku magani,
: Wayyo, uhu,
: Wayyo kur,
: Wayyo, uh! Uh! Uh!






















Adam A Zango
In Kuna Son Rawa Da Zango 
Jagora : In kuna son rawa da Zango ku ce yayye!
Karɓi : Yayye!
Jagora : In kuna son ku gan ni Zango ku ce Ushe,
Karɓi : Ushe!
Jagora : In kuna son ku samu rahama ku ce Allah,
Karɓi : Allah!
Jagora : Walale walale walale,
Karɓi : Adam ya shigo gari,
Jagora : Ya shigo gari,
Karɓi : Yaro ne adon gari,
Jagora : Yaro ne adon gari,
Karɓi : Ya shigo garin KD,
Jagora : Eh!
: A Garin Kano da kwai Naira,
Jagora : Haka ne, haka ne!
Karɓi : Sannan muna da Sarki na Zazzagawa.
: Eh!
Jagora : Haka nan take,
Amshi : Adam ya shigo gari,
  : Yaro ne adon gari,
: Ya shigo garin KD,
: A Garin Kano da kwai Naira,
: Sannan muna da Sarki na Zazzagawa.
: Eh.
Jagora : Na faɗa Ni Zango na riga na faɗa,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : In dai ilimi ne ka je Kaduna ka yo biɗa,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Mata da maza harkar ilimi babu yin faɗa,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Cibiyar Arewa Kaduna ce kar ka yo raɗa,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Sarkin Zazzau Shehu Idiris shi ma ya faɗa,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Ya ce kowa ya kama karatu ya bar faɗa,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Bar yawon banza Mahammadiyya a yo biɗa,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Eh...
Karɓi : Walale, walale walale,
Jagora : To in na ga dama, in na ga dama,
Karɓi : Ina za ka kwana?
Jagora : In na ga dama a gidan gwamna zan kwana,
Karɓi : Ka je ka kwana,
Jagora : In na ga dama a gidan sarki zan kwana,
Karɓi : In ya ba ka dama,
Jagora : Kai in na ga dama a garin Zazzau zan kwana,
Karɓi : Ka samu dama,
Jagora : In na ga dama a garin KD zan kwana,
Karɓi : Mun amunce ma,
Jagora : Eh...
Amshi : Adam ya shigo gari,
  : Yaro ne adon gari,
: Ya shigo garin KD,
: A Garin Kano da kwai Naira,
: Sannan muna da Sarki na Zazzagawa.
: Eh, yeyye, Ushe!
: Yeyye, Ushe!
: Allah, walale walale walale.
Jagora : Masarautar Zazzau ta kere sa’o’inta da dama,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : A fagen yaƙi Zazzau jarumai an yi su da dama,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Ko Ƙur’ani idan ka duba za ka gani ma,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Akwai bugun Zazzau na malamai za mu jaddada ma,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Malam je ka Kusfa da malamai za su agaza ma,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Kaduna Garin Gwamna A.A. Zango nake faɗa ma,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : In kana da Naira ka je Kaduna ka ƙera gida ma,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Lallai ka cika mai kuɗi.
Karɓi : Eh, walale walale walale,
Jagora : In na ga dama in na ga dama,
Karɓi : Ina za ka kwana?
Jagora : In na ga dama Unguwar Dosa zan kwana,
Karɓi : Je ka kwana,
Jagora : Kuma in na ga dama Unguwar Shanu zan kwana,
Karɓi : Ka samu dama,
Jagora : Kuma in na ga dama Nasarawa ni za ni kwana,
Karɓi : Ka samu dama,
Jagora : Kuma in na ga dama Tudun Wada ni zan kwana,
Karɓi : Mun amunce ma,
Amshi : Adam ya shigo gari,
  : Yaro ne adon gari,
: Ya shigo garin KD,
: A Garin Kano da kwai Naira,
: Sannan muna da Sarki na Zazzagawa.
: Eh, yeyye, Ushe!
: Yeyye, Ushe!
: Allah, walale walale walale.
Jagora : To Bisimillah,
: Na haɗa da sunan Allah,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Komai sai ka sa Allah,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Yau gani Kaduna Garin Gwamna,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Na taho na gai da gida ne,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora :’Yan Zango na gaishe gaba ɗaya,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Haɗa da Zankuwa da Zankuwa City,  
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : My people na Samunaka,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Lere da Doka har Mariri,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : ’Yan Kafanchan na gaishe ku,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Da ’yan Kaduna Ilove you people,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora :Yau ga ni a Zariya City,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Zo ka bi ni ku sha labari,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Na biyo ta Ƙofar Doka,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Ƙofar Kuyanbana, na shiga Kona, 
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Gaishe ku mutanen Ƙofar Gayan,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Ƙofar Kibo na Galadima,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Kirari : Lafiya Sarkin jikan Sarki,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Kirari : Lafiya mai  nasara,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Kirari : Lafiya kirzau
Karɓi : Eh, oyoyo,
Kirari : Sarki mai yawan kaya,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Kirari : Sarki mai tarin sutura,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Kirari : Sarki mai tarihi,
Karɓi : Eh, oyoyo,
Kirari : Sarki baban sarakuna,
Kirari : Sarkin ...
Karɓi : Eh, oyoyo,
Jagora : Eh, in na ga dama in na ga dama,
Karɓi : Ina za ka kwana?
Jagora : In na ga dama Unguwar Sarki zan kwana,
Karɓi : Je ka kwana,
Jagora : In na ga dama Badarawa ni zan kwana,
Karɓi : Na ba ka dama,
Jagora : Kuma in na ga dama cikin Kawo ni zan kwana,
Karɓi : Ka samu dama,
Jagora : Kai in na ga dama Malali ni zan kwana,
Karɓi : Mun amunce ma,
Jagora : In kuna son rawa da Zango ku ce yayye!
Karɓi : Yayye!
Jagora : In kuna son ku gan ni Zango ku ce Ushe,
Karɓi : Ushe!
Jagora : In kuna son ku samu rahama ku ce Allah,
Karɓi : Allah!
Jagora : Walale walale walale,
Karɓi : Adam ya shigo gari,
Jagora : Ya shigo gari,
Karɓi : Yaro ne adon gari,
Jagora : Yaro ne adon gari,
Karɓi : Ya shigo garin KD,
Jagora : Eh!
: A Garin Kano da kwai Naira,
Jagora : Haka ne, haka ne!
Karɓi : Sannan muna da Sarki na Zazzagawa.
: Eh!
Jagora : Haka nan take,
Amshi : Adam ya shigo gari,
  : Yaro ne adon gari,
: Ya shigo garin KD,
: A Garin Kano da kwai Naira,
: Sannan muna da Sarki na Zazzagawa.
: Eh.
: Adam ya shigo gari,
: Yaro ne adon gari,
: Ya shigo garin KD,
: A Garin Kano da kwai Naira,
: Sannan muna da Sarki na Zazzagawa.
: Eh.
: Adam ya shigo gari,
: Yaro ne adon gari,
: Ya shigo garin KD,
: A Garin Kano da kwai Naira,
: Sannan muna da Sarki na Zazzagawa.
: Eh.








Adam A. Zango
Duniya Ta Kusan Tashi
Jagora : Haka!
Karɓi : Yaf yaf yaf yaf yaf!
: Ruwan sama saka lumbayye,
Jagora : Haka!
Karɓi : Yaf yaf,
: Mai baiwa daga Allah Adam Zango.
Jagora : Yee yee ye ye yee yee!
: Duniya,
: Wayyo duniya ta zo ƙarshe,
: E, duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe,
Amshi : Duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Jagora : E, bisimilla Allah Maƙagin Sarki, wanda yay sama babu gwafa,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Shi ke yin zafi har sanyi kuma yay mana bargo mu rufa,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Shi Rabbi ke sanya ciwo ya ba mu magani nai fa duba fa,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Uh, Ka ba ni ikon aikata kari, shi ko sharri mu kakkauce fa,
: Rabbi dom ba mu kauce ba,
Amshi : Duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Jagora : E, rayuwar ta yi tsada kowa da tsarin da zai ɗabi’arsa,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Wani in ba gulma ya yo a kullum bai da ikon ya numfasa,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Wani ko burinsa ta yaya zai yi ya ƙuntata wa amininsa
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Wani ko bai ya jin daɗi sai ya yi hasada a cikin ransa,
: To hakan bai dace ba,
Amshi : Duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Jagora : A zamanin yanzu babu zumunci ya riga ya lalace,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Wani ɗan’uwa ne yake ƙauna ya ga ɗan’uwan ya susuce,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Ka ga wa da kuɗi amma ƙannensa cikin talauci a ƙasƙance,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Ka ga ɗa da uba wai ana faɗa Wallahi ɗa ka lalace,
: Jahannama ba za ta ƙyale ba,
Amshi : Duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Jagora : Wani sabon salo da bawa ke yi gun mace in ya je zance, 
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Um, sai ta sa hijabi ta saka shi ciki da sunan suna zance,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Sai kai ɗaya ƙafa guda huɗu a duhu zuciya ta gurɓace,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Da ka fara zuwa ba ka yin haka sai ta ce kai gara kauce,
: Wane sam bai gane ba,
Amshi : Duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Jagora : E, irin gine-ginen da ake ta yi fa a duniyar ga ban gane ba,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Ka ga Ɗan’adam da mota saba’in shi kaɗai kamar ba za su ƙare ba,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Ginin gida ko ya zarta ɗari kai ka ce ba za su rushe ba,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Um ka ga uwa tana hana ’yarta zaman aure dom ba mai kuɗi ba,
: Mai yin hakam ba ta kyauta ba,
Amshi : Duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Jagora : Haka! X2
Karɓi : Yaf yaf yaf yaf yaf!
: Ruwan sama saka lumbayye,
Jagora : Haka!
Karɓi : Yaf yaf,
: Mai baiwa daga Allah Adam Zango.
Jagora : Yee yee ye ye yee yee!
: Duniya,
: Wayyo duniya ta zo ƙarshe,
: E, 
Amshi : Duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Jagora : E A yau idan muka duba kwaɗayi yay yawa ba mu gane ba,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Um ba za ka aurat da ’yarka ba wai mai kuɗi kake hangowa,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Budurwa ta yi ta zama a gida kullum tana ƙara tsofewa,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Da ka je gun yarinya ta gane ba Dala sai ta zuƙewa,
: Ba zan soyayyar wahala ba,
Amshi : Duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Jagora : Shi ne ya sa ga shi mata sun fi maza yawa sun ninninka
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : In za a bi kowa da goma-goma ragowar sai su ninninka,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Komai zurfin addininka in ba kuɗi za su ƙyale ka,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Um kana ji kama gani mai mota zai raba ka da bebinka,
: Ko bai karatun salla ba,
Amshi : Duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Jagora : A ɓangaren maza mu ma matsala ce da mu ba ’yar ƙalilan ba,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Wani in macen ba shigar banza ba ta yi wai shi ba ta waye ba,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Ya za ki rinƙa ha’inta ta ki sa hijab ban gane ba,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Wani saurayi in ya je zance ta ƙi yai kis ba za ya koma ba,
: Wance sam ba ta waye ba,
: Alla!
Amshi : Duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Jagora : Wani mai gidan a kullum a cikin matansa kullum sai ya fifita,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Ran kwanan ɗakin amarya tsire zai sayo da yajin citta,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Ita ko uwar gida ran kwananta tuwonta shi ne namanta,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Um da dafe amarya ta ci Indomi da ƙwai ɗayar ko ya ƙyale ta,
: Tun da ba sabuwa ce ba,
Amshi : Duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Jagora : Allah Sarki ina roƙo ka fitar da ni sharrin masharranta,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Ka tsare ni ganin ƙyashin kowa ka guje ni yi wa kowa ƙeta,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Ka ƙara min son ManzonKa da masoyina in ma bauta,
Karɓi : Duniya ta zo ƙarshe,
Jagora : Da na ji zan yi wa wani kushe to zuciyata ka kulle ta,
: Ta yarda ba zan buɗe ba,
Amshi : Duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Jagora : Eh duniya ta kusan tashi amma mutum bai gane ba,
: Duniya ta zo ƙarshe.
Karɓi : Yaf yaf yaf yaf yaf!
: Ruwan sama saka lumbayye,
Jagora : Haka!
Karɓi : Yaf yaf,
: Mai baiwa daga Allah Adam Zango.
Jagora : Haka!
Karɓi : Yaf yaf yaf yaf yaf!
: Ruwan sama saka lumbayye,
Jagora : Haka!
Karɓi : Yaf yaf,
: Mai baiwa daga Allah Adam Zango.











Adam A. Zango
Sarkin Zazzau Hanjin Jimina
Sanƙira : Gyara kimtsi,
: Gaba salamun baya salamun.
: Hadari sa gabakanka inda kake so Yariman Mawaƙa,
: Mu je zuwa, aha!
Jagora : Adam Zango mai gari,
: Yaro ne adon gari,
: O’o o, o’o o, oo,
Sanƙira : Toh, toh, to!
Amshi : Ga kambun mafarauta,
: Dogon barde hancin giwa.
Jagora : Ga mai darajar farko matsayi,
: Sarkin Zazzau hanjin jimina,
Karɓi : Kowa ya ci sai ya lalace,
: Matsayinka daban babban sarki.
Jagora : Kai duk tsananin ramar doki,
Karɓi : Kofato na nan bai ramewa,
: Haka Rabbi yake aje hikimarsa,
Jagora : To ga Sarkin Zazzau,
: Shehu Idiris mai takalman ƙare,
: Toh,
Amshi : Ga kambun mafarauta,
: Dogon barde hancin giwa.
Jagora : Ga mai darahar farko matsayi,
: Sarkin Zazzau hanjin jimina,
Karɓi : Kowa ya ci sai ya lalace,
: Matsayinka,
Jagora : Um!
Karɓi : Daban babban sarki.
Jagora : Ga mai ƙarfi Dagacin mutuwa,
Karɓi : Sankace da maciji dauji kar,
: Sarkin Zazau tafiya sannu,
Jagora : Um!
Karɓi : Ga gamji mazajen alfarma,
Jagora : Farko da na sauka garin Zazzau,
: Na yi ado na sa kubta,
: Na hau doki na sarauta,
Rawani kuma an muni mai kima,
Karɓi : Toh,
: Za shi gidan babban sarki.
Jagora : Kai Tasi’u saurara ka jiya,
: Da na sauka garin Birnin Zazzau,
: Na ga kalar matan Zazzau,
: Da ado tamkar matan Makka,
: Ga shi ina son mu yi hira,
: In ji labari na gidan sarki,
Karɓi : To amma kuma sam ba dama,
: Musulunci bai yarje ma ba.
Jagora : Um!
Karɓi : In ka bi ta zancena.
Jagora : Me ya sa na ga matan Zazzau,
: A ado sun zarce sun kera,
Karɓi : To ko tarihin tafi ɗauko,
: Sarauniyar Zazzau a Arewa,
: Ba wanda ya kai ta ajin girma.
Jagora : To gani gaban fadar sarki,
: Sarkin Zazzau mai alfarma,
: Toh,
Amshi : Ga kambun mafarauta,
: Dogon barde hancin giwa.
Jagora : Ga mai darahar farko matsayi,
: Sarkin Zazzau hanjin jimina,
Karɓi : Kowa ya ci sai ya lalace,
: Matsayinka,
Jagora : Um!
Karɓi : Daban babban sarki.
Jagora : Farfesun kunama sun san ka,
: Matsayinka daban babban sarki,
Karɓi : Kowa ya ci sai ya lalace,
: Matsayinka,
Jagora : Um!
Karɓi : Daban babban sarki.
Jagora : Yau ga ni gaban gidan sarki,
: Ina tafiya ta cikin ƙawa,
: Wai ni da zan shiga fada,
: Kamar ɗaki na ka ji wawa,
: Ko da na zo bakin ƙofa,
: Sai fadawa suka miƙe,
: Sadaukai da ido jajaye,
Karɓi : Kai gyara kimtsi bi a sannu,
: Gidan sarki ba shigifa ba,
: Jihar can Sakkwato nai zance,
Jagora : To a cikinsu akwai wani ma,
: Da babbar riga ga rawani,
: Sai na ji ya ce kai yaro,
: Ya daka mani tsawa nar ruɗe,
Karɓi : Sai munka kowa zazzaune,
: Yana mai martaba bar ka dai,
: A zatonsa kamar sarki yaz zo.
Jagora : Sai mutumin nan yam miƙe,
: Yac ce mini yaro kai taso,
: Me za kai a gidan sarki?
Karɓi : Mai martaba munka taho mu gani,
: Mun ji yanda yake adalcinsa,
Jagora : To kai yaro ya sunanka,
: Kuma kai ɗan wanne gari ne?
Karɓi : Kai Adam Zango ake ce ma,
: A Kaduna kake muka amsa mai,
Jagora : Kai Tasi’u da ba don kai ba,
: Ni ban san me zan furta mai ba,
: Toh!
Amshi : Ga kambun mafarauta,
: Dogon barde hancin giwa.
Jagora : Ga mai darajar farko matsayi,
: Sarkin Zazzau hanjin jimina,
Karɓi : Kowa ya ci sai ya lalace,
: Matsayinka,
Jagora : Um!
Karɓi : Daban babban sarki.
Jagora : To sun ƙyale duk sun yarje,
: Na shiga hanya na miƙe,
: Zan je fadar mai Zazzau,
Karɓi : Sai dai kuma ba ka san hanya ba,
: Gidan sarkin da akwai girma.
Jagora : Sai na ga al’umma zaune,
: Sun sha kaya na mutunci,
: Na yi tunanin baƙi ne,
: Ashe duka bayin sarki ne,
Karɓi : To ya riƙe daraja kimarsu, 
Jagora : Um!
Karɓi : Kamar ma ba bayi ne ba.
Jagora : Da na je ni gaba na gaishe su,
: Su kuma duka sun amsa,
: Bayan kowa ya yi shuru,
: Sai na ciro magana ƙwara,
: Ni dai farko baƙo ne,
: Na zo fadar sarki ne,
: Shin ko ku ne ’yan fada?
: In kuma ku ne ’yan fada?
: Ya za a yi sarki in gan shi?
Karɓi : A’a ba mu ne fada ba,
: Ga fadar can gefen hauni,
Jagora : Sarkin Zazzau mai girma,
: Ɗawisu adon tafiya kai ne,
: Toh!
Amshi : Ga kambun mafarauta,
: Dogon barde hancin giwa.
Jagora : Ga mai darajar farko matsayi,
: Sarkin Zazzau hanjin jimina,
Karɓi : Kowa ya ci sai ya lalace,
: Matsayinka,
Jagora : Um!
Karɓi : Daban babban sarki.
Jagoa : To ga ni cikin fadar sarki,
: Wazirin Sarki na zaune,
: Ga Hakimai duka na zaune,
: Ga Fadawa na zaune,
: Sai na ga wani ɗan dattijo,
: Mai siffa kamar Balarabe,
: Ya ci ado da alkyabba,
: Ga ƙamshi mai tashin ƙawa,
: Toh!
Karɓi : Allah kare sarki,
: Ɗan Idirisa daɗo girma.
Jagora : A gaban sarki na taho na zube,
: Ina ta kirari a gabansa,
: Kura mai firgita kalbu,
: Ganga mai fatar giwa,
: Ƙarko da nagarta shi an nan,
: Fage na yaƙi sai sulke,
: Duka da bugu sai ’yan barka,
: Munjirya ka wuce kamun yaro,
: Ko babba yana shakka,
: Karya gwafa shahon ƙarfe,
: Jifa a cikin ruwa shirme ne,
: Adon sama’u kake sarki,
: Zara kake mai taurari,
: Mu dai sai sa albarka,
: Buzun bushiya ba a imma,
: Kai ni Zango a wurina,
: Duk sarakuna ai ka fi su,
: Toh
Amshi : Ga kambun mafarauta,
: Dogon barde hancin giwa.
Jagora : Sarkin Zazzau mai girma,
: Ɗawisu adon tafiya kai ne,
: Toh!
Karɓi : Allah kare sarki, 
: Ɗan Idirisa daɗo girma.
Jagora : Daga nan shauƙi yak kwashe ni,
: Na ci gaba da kirarin mai girma,
Karɓi : Sarari mai ƙare gudun doki,
: Tsawa sa karkarwa.
Jagora : Toh, toh!
Karɓi : Tsakar dare hana tafiya,
: Ragayar dutse ajalin yaro.
Jagora : Um!
Karɓi : Allah kare sarki, 
: Ɗan Idirisa daɗo girma.
Jagora : You are the man of the people,
: You are the last man standing,
: You are the almighty king,
: Shin a Arewa kuwa dak kamarsa?
: Toh!
Karɓi : Kai Zango ka saita batunka,
: Don kana gaban sarki ne.
Jagora : Bari Tasi’u sai na ƙara, 
: He is the greater than Sarakuna,
Karɓi :  You are special ɗan Zango,
Jagora : Well done,
Karɓi : Turancin sai mun ɗana.
Jagora : Rabi kare Sarkin Zazzau,
: Mai martaba ubana babba,
Amshi : Ga kambun mafarauta,
: Dogon barde hancin giwa.
Jagora : Ga mai darajar farko matsayi,
: Sarkin Zazzau hanjin jimina,
Karɓi : Kowa ya ci sai ya lalace,
: Matsayinka,
Jagora : Um!
Karɓi : Daban babban sarki.
Sanƙira : Gyara kimtsi,
: Gaba salamun baya salamun.
: Hadari sa gabakanka
: Yariman mawaƙa mu je zuwa
: Ahah!
Jagora : Adam Zango mai gari,
: Yaro ne adon gari,
: O’o o, o’o o, oo,








Adam A. Zamgo
Tsumagiya
Jagora : Tsumagiya!
Amshi : Gumban dutse,
: Igiyar ruwa mai sartse,
: Ragayar dutse,
: Ajalin mai ɗaki sai jigo.
Jagora : Toh, toh, toh!
: Shi ɗan Adam mai cin zali nasa,
: Na sama ke take na ƙarƙasa,
: Babu imani a zuciyarmu,
: Yanzu kowa tasa yake,
Karɓi : Tasa,
: Kun ji Adam Zango,
Jagora : Um!
: Zantuka zai ƙirgo,
Jagora : Um!
Karɓi : Ku saurara ku ji zancensa,
Jagora : Toh, toh, toh!
Karɓi : Abin da Zango ya hango.
Jagora : E.. na faɗa na ƙara,
: Ɗan’adam ba ya tsoron Allah,
Karɓi : Um!
Jagora : Sannan a cikinsu ƙalilan,
: Wasu ke aikin Allah
Karɓi : Um!
Jagora : Wasu sun samu duniya,
: Suna ta ɗibar daula,
Karɓi : Um!
Jagora : Wasu ko ba su da komai,
: Kullum idonsu da ƙwalla, 
Karɓi : E, mutaimaka don Allah,
Jagora : Wayyo!
Karɓi : Mu so juna da amana.
Jagora : Um!
Karɓi : Sannan mu zauna lafiya.
Jagora : Aha!
Karɓi : Mu canza halayenmu,
: Saboda rayuwar ga ba ta da tabbas,
Jagora : Eh...
Amshi : Gumban dutse,
Jagora : Toh,
Karɓi : Igiyar ruwa mai sartse,
Jagora : Uhum!
Karɓi : Ragayar dutse,
: Ajalin mai ɗaki sai jigo.
Karɓi2 : Um! Malam Adam Zango,
: Ga tambayata zan yi maka,
: Rayuwa da akwai matsala,
: Da me da me fa ka fuskanta.
Jagora : Kai, El-Mu’az bari zancen nan!
: Rayuwarmu akwai muni,
: Kowa duk ya juye,
: Hausawa sun juye,
: Yaren ma duka sun juye,
: Ka ga ’ya ta bunƙasa,
: Ba aure sai dai yawo,
Karɓi2 : Kai dakata Malam Zango,
: Ai laifin na samari ne!
Jagora : A’ a’a na iyaye ne,
: Wasu sai ka ga sun ba ’ya’ya,
: Na ta ɗaukan nauyinsu,
Karɓi2 : To hakan wai baiwa ce?
Jagora : Kai El-Mu’az wace baiwa ce,
: Za ka ga ’yarka cikin daula, 
: Ba ka san sana’arta ba ma,
: Za ka ga wai ta sai Hala,
: Rayuwa sai lahaula!
Karɓi : Adam Zango akwai illa?
Jagora : E, tabbas fa akwai matsala,
: Burin kowa dai daula,
Karɓi : Kai
: Gumban dutse,
Jagora : Toh,
Karɓi : Igiyar ruwa mai sartse,
Jagora : Uhum!
Karɓi : Ragayar dutse,
: Ajalin mai ɗaki sai jigo.
Jagora : Eh... iyaye dole ku yo tsari,
: Ku dinga bincika ’ya’yanku,
: Ko yo tarbiyyar ’ya’yanku,
: Waɗannda  Allah yab ba ku,
: Ku ƙaunaci ’ya’yanku,
: Sai Allah ya ji tausanku.
Karɓi : Yarima fa ɗan Zango,
: Wasu sun ce ka kwafsa,
: Wai don ka faɗi halinsu.
Jagora : Kai ƙyale su da shirmensu,
: Da ma kowa ya san su,
: Mai son ya ji sunansu,
: Ya bi ni zan zazzano su,
Karɓi : A’ a’a Zango da ka bar su,
: Do ni ma ai na san su,
Karɓi2 : Zango mai zamani,
: Ya ka ga wannan zamani?
Jagora : El-Ma’az da ka bar ni,
: Halayen fa akwai muni,
: An yarda akwai ƙaddara,
: Ta zo sai fa a ce Allah,
: Gidanka da ya ƙone,
Karɓi : Ka ji an ce yin haka sai Allah!
Jagora : Motarka da an sace,
Karɓi : Ka ji an ce yin haka sai Allah!
Jagora : Ga wani ya rasa matarsa,
: Ga wani ya rasa ’ya’yansa,
Karɓi : Sai a gaya maka yin haka sai Allah!
Amshi : Gumban dutse,
Jagora : Toh,
Karɓi : Igiyar ruwa mai sartse,
Jagora : Uhum!
Karɓi : Ragayar dutse,
: Ajalin mai ɗaki sai jigo.
Karɓi2 : Malam Zango,
: Wai ya zancen Naira?
Jagora : To in ka yi kuɗi yanzu,
: Ba a gaya maka sai Allah,
: Sai a ce ai mun san shi,
: Da can ba shi da ko sisi,
: Daga ya bi su Lasisi Abuja,
: Kila suka sisi,
: Ko jini ko kan yaro,
: Ko kuma an bi ta bayan shi,
Karɓi : Ka ji sun mata akwai Allah!
: Da ya yay talauci yay daula.
Jagora : E...
Karɓi : Kun ji Adam Zango,
Jagora : Um!
Karɓi : Zantuka zai ƙirgo,
Jagora : Um!
Karɓi : Ku saurara ku ji zancensa,
Jagora : Toh, toh, toh!
Karɓi : Abin da Zango ya hango.
Jagora : E.. ka ga zance addini,
: Abin ya canza kalar launi,
: Da Bahaushe ya ɗauka,
: Cewa shi ne mai addini,
Karɓi : A’a wanda duk ko ya ɗau Allah,
: Da Muhammadu manzonsa,
: To Musulunci ne tsani.
Jagora : Idan Iyamuri na salla,
Karɓi : Sai ka ji an ce wai tubabbe ne,
Jagora : Katafawa na salla,
Karɓi : Sai ka ji an ce tuba ne,
Jagora : Idan Igala ya ce Allah,
Karɓi : Ka ji an ce sabon tuba ne,
Jagora : In ka ga ɗan TV na salla,
Karɓi : Shi ma sai ka ji tuba ne,
Jagora : E, to ku sani a gurin Allah,
: Dukkaninku Musulmi ne,
: ’Yan’uwan kuma juna ne,
: Ƙur’aninmu guda ɗaya ne,
Karɓi : Eh
: Kun ji Adam Zango,
Jagora : Um!
Karɓi : Zantuka zai ƙirgo,
Jagora : Um!
Karɓi : Ku saurara ku ji zancensa,
Jagora : Toh, toh, toh!
Karɓi : Abin da Zango ya hango.
Jagora : Eh..
Amshi : Gumban dutse,
Jagora : Toh!
Karɓi : Igiyar ruwa mai sartse,
Jagora : Uhum!
Amshi : Ragayar dutse,
: Ajalin mai ɗaki sai jigo.
Karɓi : Adamu ya maganar waƙa,
: Don wasu sun ce shirme ce?
Jagora : Kai waƙa ai baiwa ce,
: In ka iya ta ko ka dace,
: Don jahili ba ya waƙa,
Karɓi : Wasu sun ce laifi ce,
: Da ka fara ta ka kauce?
Jagora : Kai ƙyale duka sun zauce,
: Sana’ar waƙa ilimi ce,
: In ka tsaftace harshenka,
: Ka gyara tunani ka dace,
Karɓi : Na gane tunaninka,
: Zango ni ma na auna.
Jagora : Ai kowacce irin sana’a,
: Za ka samu wutarka da aljanna,
: Gatan Zango waƙa,
: Ilimin Zango waƙa,
: A cikinta ko nai jari,
: Kuma ba na yin ƙari,
: Kai gorin ilimin boko,
: Ni kuma Zango akwai jari,
: Sana’ata ga tsari,
: Ni na yo ilimin bokon,
: Ƙarshe waƙa ce jari,
: Kai ku ji Allah mai khairi,
Karɓi : E Zango dodon waƙa,
: Me za ka ce wa abokanka?
Jagora/ : Allah shi muku albarka,
Karɓi : Mai barci kuma yaf farka,
: Im mun ilimin bokon,
: Sana’ar hunnu mu ɗan kama,
: Wani walda yak kama,
: Waɗansu su je su yi kafinta,
: Wasu na gyaran famfo,
: Waɗansu na aikin doki,
: Wasu ’yan fim ne malam,
: Waɗansu na harkar waƙa,
: Wani na ɗaukar hoto,
: Waɗansu na turin baro,
: Wanda duk ya riƙe sana’a,
: Allah kai masa kai albarka,
: Don wata rana ya zam zaki,
: Nan shi ne ƙarshen waƙar
Sa ido sana’ar banza!


 












Adam A. Zango
Sharafi
Jagora : Eye, ku zo ku ji tarihina,
: Labarin yaro Ado,
: Sharafi, sharafi,
Amshi : Ku zo ku ji labarin,
: Tarihin yaro Ado, 
: Yaro mai sharafi,
: Sharafi sharafi.
Jagora : Ga ta nan ga ta nanku,
Karɓi : Ta zo mu ji ta,
: Sharafi.
Jagora : Ku sani dai,
: A Kaduna State aka haifan,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Gari na mahaifa,
: Zango ne shi ne taken,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Tun ina ƙaramina,
: Abbana ya yi macewa,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Allah ka jiƙan,
: Ibraahima can a kushewa,
Karɓi : Allah amin.
Jagora : Ina gani da idona,
: Tarzoma an yi a gabana,
Karɓi : Allah ya kiyaye,
Jagora : Ina kallo,
: An kashe yayyena a gabana,
Karɓi : Allah ka jiƙansu da gafara.
Jagora : Don haka ne,
: Nak koma Jos gun kawuna,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Can nai makaranta,
: Boko har ma Islama,
: Sharafi,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
: Yaro mai sharafi.
Amshi : Ku zo ku ji labarin,
: Tarihin yaro Ado, 
: Yaro mai sharafi,
: Sharafi sharafi.
Jagora : Na kamala sakandare,
: Sai karatu yay y tsayawa,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Ba aikin yi,
: Babu kuɗin da zan yi kashewa,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Sai nai yi tunani,
: In shiga fim ɗin Hausa,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Sai na tattara kayana,
: Nat tafi tashan mota,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Sai direba ya ce min,
: Wai ina za ka je Ado?
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Sai na ce garin,
: Mai Martaba Sarki Ado,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Kanon Dabo,
: Ko da mai ka je an fi ka,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Sai ga ni Fage,
: Na sauka gidan innata
Karɓi : Yaro mai sharafi.
: Yaro mai sharafi.
Jagora : Sharafi sharafi,
Amshi : Ku zo ku ji labarin,
: Tarihin yaro Ado, 
: Yaro mai sharafi,
: Sharafi sharafi.
Jagora : Washe gari na je,
: …
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Lense Cope Media, 
: Gun Salisu Mu’azu,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Nas same shi,
: Salisu yai mini marahabin,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Ya ba ni abinci, 
: Na ci nai ƙat ban manta ba,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Bayan na huta, 
: Ya ce kai Adam Zango!
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Me ya kawo ka, 
: Mene ne kaz zo yi nema?
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Na ce Oga, 
: Na zo ne nai fim ɗin Hausa,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : In zama kamar,
: Ali Nuhu ko S. Nuhu,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Sai yai dariya, 
: Ya ce Allah zai yi ma,
: Sharafi,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
: Yaro mai sharafi.
Jagora : Sharafi sharafi
Amshi : Ku zo ku ji labarin,
: Tarihin yaro Ado, 
: Yaro mai sharafi,
: Sharafi sharafi.
Jagora : A kwana a tashi,
: Sai ga ni ina yin kiɗa,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : A kwana a tashi,
: Sai ga ni ina yin waƙa,
Jagora : A kwana a tashi,
: Sai ga ni a fim ɗin Hausa,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Har na yi suna, 
: Na kere sa’annina,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Jama’a sun sanni,
: Duk mai kallon fim ɗin Hausa,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Kowa ya sanni, 
: Idan yana jin waƙar Hausa,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : Ai dole ka sanni,
: Idan kana jin kiɗin Hausa,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : A fage na kiɗa, 
: Danko ai shi ne ogana,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : A fagen waƙa, 
: Bily O ne ogana,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora : A fagen shirin Hausa, 
: Ali Nuhu ne ogana,
: Sharafi,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Amshi : Ku zo ku ji labarin,
: Tarihin yaro Ado, 
: Yaro mai sharafi,
: Sharafi sharafi.
Jagora : Na zauna da mutane,
: Masu ɗimbin ƙauna ta,
Karɓi : Yaro mai sharafi.
Jagora :  Ali Nuhu,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Auwal MD,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Salisu Mu’azu,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora :  Ibrahim Danko,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Naziru Hausawa,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Maryam Mashhama,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Kalil Jamani,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Kalid Kachiya,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Falalu Ɗorayi,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Mai gaskiya,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Safiya Musa,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Tijjani Asasi,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Tahir I Tahir,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Baban Chinedu,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Mika’il Gidigo,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Umar Kanu,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Awwal Isa West,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Tijjani Albasha,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Mansur Sadik,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Lawal Ahmad,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Tijjani Kazaure,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Abubakar Sani,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Jamil Kazaure,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Aminu Sulpur,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Maryam Sangandali,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Jamilan Sadi,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Azazi SB Jakara,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Abubakar Hunter,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Jamilu Kochila,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Saifullahi,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Mukhtar Uzi,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Sharu na Gudu,
Karɓi : A Zango yana gaishe ku.
Jagora : Lawan Alasan Ƙaura,
: Sharafi,
  Amshi : Ku zo ku ji labarin,
: Tarihin yaro Ado, 
: Yaro mai sharafi,
: Sharafi sarafi.
Jagora : Ku zo ku ji tarihina,
: Labarin yaro Ado,
: Sharafi, sharafi,


Comments

Popular posts from this blog

Ranar Hausa

Ranar Hausa Ta Duniya Inda Gizo Yake Saƙarsa: Hausa Ci Gaban Mai Ginan Tukwane Ko Ci Gaban Mai Haƙar Rijiya? 26/08/2023 Shin wannan ba son uwar dawa kawai ake yi wa harshen Hausa ba, har ma da romon baka. Akwai rubuce-rubuce da yawa da aka yi cikin harshen Hausa da suka haɗa da: Rubutattun waƙoƙin Hausa Waƙoƙin baka Rubutattun waƙoƙi na zamani Waƙoƙin baka na zamani Rubutaccen wasan kwaikwayo Wasan kwaikwayo na rediyo da na talabijin da na kuma bidiyo Wasan kwaikwai mai JERENGIYA (mai goyo ko mai dogon zango) Jaridu da mujallu na Hausa Gidajen rediyo da na talabijin da ake gudanar da su da Hausa Jami’o’i da kwalejin ilimi da na kwalejin kimiyya da fasaha da ake nazarin Hausa Sai dai wa ke karantar Hausa a mataki na JAMI’A ko KWALEJIN ILIMI ko KWALEJIN KIMIYYA DA FASAHA? Wa ke so ɗansa ya karanta Hausa a kowane irin mataki? Me ya sa a lokacin ɗaukar jarrabawar SAKANDERE yaranmu ba sa so su sanya Hausa a cikin jerin takardun da suke so su rubuta? Me ya sanya a swance ko ...

Hausa Karin Magana

29/11/2019 Duk wanda ya ɗauki namiji uba, zai mutu maraya. Duk wadda ta ɗauki namiji uba, za ta mutu marainiya. Duk wanda ya ɗauki namiji uba, za ta mutu ba a mata gara ba. Namiji ba ɗan goyo ba.  Salon Tsari Na Karin Maganar  Duk waɗannan karin maganganu ne na Hausawa kuma sun hau kan tsari. Idan aka duba za a ga karin magana ce mai ɓarayi biyu: Sashen farko: Duk wadda ta ɗauki namiji uba, = gaɓoɓi 11 Sashe na biyu: Za ta mutu mareniya. = Gaɓoɓi 8 Duk wadda ta ɗauki namiji uba/ za ta mutu marainiya. 11/8 Wannan salo ne da zubi na karin maganar Hausa, wani lokaci za a ga sashen dama ya fi yawan gaɓoɓi, wani lokaci kuma hagu ya fi yawa, a wasu wuraren kuma su zama ɗaya, amma kuma za a ga ma’ana ta tafi yadda ake so ba tare da ta ɓaci ba. Yadda Ake Amfani Da Karin Maganar Mata su suka fi amfani da wannan karin maganar, kuma suna amfani da ita ne a lokacin da namiji ya yi masu ba daidai ba, sai su faɗi wannan karin maganar da nufin su nuna masa cewa, ai da ma suna san...

JERIN SARKE A WAKOKIN BAKA NA HAUSA NA MUHAMMAD BELLO FALAMA 2015

Babi Na Ɗaya Gabatarwa 1.1      Shimfiɗa Waƙa, walau ta baka ko rubutacciya, wani muhimmin ɓangare ne na adabin al’umma. Masana sun yi nazarce-nazarce da dama kan jigo da salo, da kuma zubi da tsarin ire-iren waƙoƙin da ake da su na Hausa. Ta fuskar irin waɗannan nazarce-nazarce ne aka gano saƙonni da salo da kuma zubi da tsari da ma wasu abubuwa na daban da suka ƙunsu a cikin waƙoƙin baka na Hausawa. Wannan nazari ya ɗora ne a kan ire-iren nazarce-nazarcen da aka yi kan waƙoƙin baka na Hausawa, inda aka ɗauki jerin sarƙe aka nazarce shi. An ga yadda yadda maimai ke taka rawa wurin haifar da jerin sarƙe nau’o’insa. Jerin sarƙe, zance ne wanda aka sarƙa a falan biyu ko fiye, wato inda aka samu daidaito na sunaye ko yankuna ko kalmomi ko aka samu wani irin zubi mai burgewa, da aka samu ɓuraɓusai a cikinsa. An yi bayanin nau’o’in jerin sarƙe da suka haɗa da “Cikakken Jerin Sarƙe” da kuma “Ragagge Jerin Sarƙe”, tare da la’akari dadalilan da suke haif...