Jarumar Mata
Hamisu Breaker
Shifta: Sarki Falama
Laraba 24/06/2020
https://youtu.be/Cq_Gz7f0rgU
1
Ashe da rai nake son ki‚
Jaruma ba da zuciyata ba.
2
Komai ruwa da iska‚
A kanki ba za na daina kewa ba.
3
Idan na samu zarrar samunki‚
Ba za na tanka kowa ba.
4
Ni ban ga mai harara ba‚
Bare na waiwaya ba.
5
In dai a kanki ne za na jure‚
Wahalar zuwa garin nisa.
6
Da an taɓa ki a jira ni don ko‚
Tilas na zo na ɗau fansa.
7
Jimirin jiranki nai don ki zo‚
Na kalle ki Gimbiyar Hausa.
8
Sirri na rayuwata ke ce‚
Kamar kin kira da na amsa.
9
Zuma a baki daɗi gare ta‚
Kin ba ni taki na lasa.
10
In dai a kanki ne na yi nisa‚
Don ba kiran da zan amsa.
11
Tilas ganinmu tilas barinmu‚
Ƙaunarki tun da nai nisa.
12
Sam ba batun na fasa‚
Ko za a ce min im ba da rai fansa.
13
Tsarin zubinki daidai ne‚
Ya kama zuciyata ne‚
Ina jin kamar mafarki ne‚
Ina son ki so mataki ne.
14
Ni ban da damuwa‚
In har zan buɗe ’yan idanuna‚
In kalle ki ga ki dab da ni‚
To me za ya damu ƙalbina.
15
Yau za ni yo amo tun da‚
Na gane kina da tausaina.
16
Don yanzu na zamo ya,
Mafatauci mai biɗar gurin kwana.
17
Na ƙwalla shela don sanar‚
Da iya maƙƙiya kalamaina.
18
Daga zuciya nake kwatancen‚
Ina zayano jawabaina.
19
Idan babu ke ina ne zan sanya‚
Zuciya ta bar yawan ƙuna.
20
Kowa da nasa amma‚
Ni ke ce cikar muradaina.
21
Yau gani har ruwa kusa da,
Kada zo ki ceci ƙarkona.
22
Komai da maffita kar da‚
Ki saɓa da furta ban kwana.
23
Ina ji ina gani‚
Yadda nake son ki ya fi ƙarfina.
24
Na san a duniya‚
Da wanda yake janye duk tunanina.
25
Soyayya rayuwa‚
Wani sa’in sai ta zan wutar ƙuna.
26
Duk wanda ke cikinta
Shi ne jurau amma fa a gurina
27
So na faranta rai da ruhi‚
Ya sa ka zam kamar sarki
28
Kuma rayuwa da so
Misali zaina kama da a mafarki.
29
Samari mui haƙuri
Idan har mun samu so mu sa sauƙi.
30
’Yam mata mui haƙuri
Idan har mun samu so mu sa sauƙi
31
Masoyi yana da rana ne
Masoyi yana da rana ne
Masoyi yana da rana ne.
Wannan fassara ta fita tsaf
ReplyDeleteIna godiya
DeleteIna godiya
Delete