MAHIRU KO FARFESA
Mahiru
Gangaran da ya bauta wa Ƙur’ani har ta kai da ya san wasu sirrora na Ƙur’ani da ba kowa ya san su ba. Ya yi saukan satu ya kuma rubuta Ƙur’ani ya kuma dade yana koyarwa yana ja ana ja da shi har dai aka gane ya wuce Gangaran, har a zo ana raɗe-raɗin kai wannan fa ya kai Mahiru, daga nan sai kowa ya sake masa.
Mahiru ko ya yi kuskure madiba kasa gyara masa suke yi domin suna tunanin gwada su yake ko suna tsoron ƙulumboto irin nasu. Kuma da sun ji ya dawo ya gyara sai ransu ya yi daɗi, saboda ba a so ana karanta Ƙur’ani da kuskure. In Mahiru yana karatu ya yi kuskure ko da kowa bai gane ba, kai ko da ya kai ƙarshen karatun ne zai dawo ya gyara kayansa da kansa, sai ka ji masu saurare suna kai jinjina suna “um”, in kuma ya ga dama zai iya cewa zai yi karatu ba kuskure kuma hakan za ta kasance, in kuma wani na karatu zai iya gane cewa zai yi kuskure, zai iya hana wani ya yi karatu, ko ya sa kasa.
Mahiru zai iya fitar da harji na ayoyi, kuma gwani ne ga mairam. Sannan wata babbar baiwa tasa ita ce, idan aka rubuta Ƙur’ani aka kawo masa don gyara, wani lokaci ma ba sai ya karanta ba, kawai zai riƙe ne da hannu ya jinjina daga nan sai ya faɗi duk wani kuskure da ke ciki da shafi da yake, kawai zai kwatanta ne, kana buɗawa za ka gani.
Mahiru ba ya shiga musaffa saboda ba wanda zai iya takara da shi, sai dai wani lokaci yakan ziyarci mahiru ɗan’uwansa su yi musaffa irin nasu na gwanaye, irin wannan musaffa abin kallo ne, kuma sai su suka iya kayansu, saboda wani lokaci sukan karanta Ƙur’ani da karatun babbaƙu ko farfaru wannada ba kowa ke iya wannan ba.
In Mahiru ya ga dama yakan rubuta Ƙur’ani amma sai ya fara da yin wasula da ɗige-ɗige na baƙi daga bisani kuma sai ya zo ya riƙa sassaƙala baƙaƙe.
KAI AIKIN MAHIRU SAI SHI, DON BA KOWA BA NE ZAI JI YA YARDA, KO YA CE WANNAN ABU BAIWA CE DAGA ALLAH! KAI DAI KA JI KA SAN AKWAI MASU YI, WANDA SU SUKA SAN HANYAR DA SUKE BI SU AIKATA IRIN HAKA
FARFESA
A bokonce, mutum ne da ya wuce matakin digiri na uku ya ƙara da wasu bincike-bincike. Farfesa malami ne da ke zaune a ƙarƙashin SASHE na TSANGAYA a JAMI’A da ya karantar da ɗalibai tun daga matakin digiri na farko har zuwa digiri na uku, aka ba shi ɗalibai a waɗannan mataka ya duba kundayensu na bincike ya yi gyara a cikinsu. Ya gabatar da maƙaloli na bincike a gida da kuma waje. A wasu lokutan ma yakan yi aron fadama ya shiga fagen da ba nasa ba ya yafuto wani abu ya kuma gabatar. Malami bai zama farfesa sai ya zama tirkakke a wata jami’a.
MUHAMMAD BELLO FALAMA
BARKANMU DA SALLA
02/09/2017
Comments
Post a Comment