Wasu Hikimomin Da Ke Cikin Camfin Hausawa
“Duk Wanda Aka Shere Shi, Zai Rasa Mata!”
Camfi wata dabara ce ta tarbiyya da Hausawa ke amfani da ita wurin shiryar da ’ya’yansu ba tare da sun faɗa masu madogara ba, saboda ganin cewa su yara ne, ko gaya masu madogarar ba ta da wata fa’ida, ko kuma in an gaya masu ƙwaƙwalwarsu ba za ta ɗauka ba.
Camfi shi ne a ce, idan abu kaza ya faru, to, lalle ne abu kaza shi ma ya faru. Misali: “Duk wanda ya yarda aka share shi, zai rasa mata”.
Tunanin da ke cikin wannan chamfin shi ne, a da aure na da wahala, shi ya sa ma Bahaushe ke cewa, “Ba neman aure ke da wuya ba, a shiga a fito”. A wasu wurare sai ka yi noma ko ka kai wa iyayen matar da kake nema gayya, wato ka tara abokanka ku je ku nome wa iyayanta gona.
Bayan wannan sai ku nemi aure ku goma sha, a ce a ciki ne za ta fitar da guda da za ta aura. Daga nan fa an riƙa kai toshi ke nan ba iyaka. Wannan ya kai nasa, wancan ma ya kai. In wannan ya ga alamar wancan ya fi shi tagomashi a wurin budurwar ya jefe shi ko ya yi masa asirin da zai nakasa shi, ko ya haukata shi. Wani lokaci kuma amaryar za a yi wa tasau a ce ba za a ɗaura auren ba sai an biya duk wani abin da ta ci na saurayi, har ma abin yakan kai ga alƙali.
Ita kuma shara da aka danganta abin da ita, da farko dai shara in ana yin ta akwai abubuwa da yawa a cikinta da ido ke iya gani, sannan akwai wanda bai iya gani. Ga guba ga ƙura wanda mai lalura idan ya tsaya a wurin da ake sharar nan, tana iya tashi.
Saboda haka, maimakon a zo ana ce maka matsa ana faɗa da kai, wani kuma girman kai ne ko haushi zai hana ya matsa daga inda ake shara. Shi ne, sai akwa kwatanta yadda kowa ke son mata in kuma mace ce miji, sai aka ce za ka rasa matar ko za ki rasa mijin.
In kuma har ka kuskura aka share ka, to akwai makari, shi ne a yi maka azaba, wato sai ka ciji tsintsiya, wanda kuma wulaƙanci ne. Ita ma ƙazama ce tsintsiyar, don ba irin abin da ba a sharewa da ita.
Da wannan sai abin ya zama da sauƙi, kai mai shara sai a ba ka wuri ka yi shararka, kai mara shara kuma an tsare lafiyarka cikin hikima. Don haka ba kare bin damo.
Muhammad Bello Falama
Comments
Post a Comment